News

Wadanda suka sace wasu fitattun jaruman Nollywood guda biyu sun nemi kudin fansa har $100,000

Wadanda suka yi garkuwa da wasu fitattun jaruman fina-finan Nollywood, Cynthia Okereke da Clemson Cornel, aka Agbogidi sun nemi dala 100,000 domin a sako su.

Idan za a iya tunawa, an ba da rahoton bacewar jaruman ne bayan da ‘yan uwansu suka tabbatar da cewa ba su dawo gida daga wurin wani fim ba a Garin Ozalla, Jihar Enugu, a ranar Alhamis, 28 ga Yuli, 2022.

Sai dai a ranar Asabar, 30 ga Yuli, 2022, shugaban kungiyar Actors Guild of Nigeria (AGN) na kasa, Emeka Rollas, ya ce masu garkuwa da mutane sun tuntubi iyalan wadanda abin ya shafa kuma suna neman zunzurutun kudi dala 100,000.

See also  Rarara Ya Bawa Mutane 6 Kyautar Motoci Ya Kuma Bawa Mutane 14 Kyautar Iphone 13 Pro Haka Zalika Ya Bawa Mutane 200 Kyautar Naira 100,000 Ga Kowanne Mutun Daya.

Rollas ya kuma ce mambobin kungiyar ta jarumai suna aiki kafada da kafada da iyalan wadanda abin ya shafa da kuma jami’an tsaro don ganin an sako su lafiya.

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button